On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

An Kori Wasu Ma'aikatan Gwamnati Sabo Karbar Albashi Biyu A lokaci Daya A jihar Ondo

GWAMNA ROTIMI NA JIHAR ONDO

Gwamnatin Jihar Delta ta amince da aiwatar da kaso na biyu na shirin koyawa matasa sana’oin dogaro da kai a karkashin tsarin fasahar sadarwar zamani wanda Ma’aikatar Kimiyya da fasaha ta kasa ke kula dashi.

Sakataren Yada Labarai na gwamnan jihar, Olisa Ifeajika ne ya baiyana haka a fadar gwamnatin jihar, lokacin da yake yiwa manema Labarai jawabi, jim kadan bayan kammala zaman majalsiar zartarwar jihar wanda gwamna Ifeanyi Okowa ya jagoranta.

Yace Matasa Kimanin Dari Biyar da Saba’in Da Biyar ne zasu amafana da shirin a karo na biyu  wanda mutane  25 daga kowace karamar hukumar ta jihar 23 zasu amfana.

Sai dai kuma yace takardar shaidar Diploma itace mafi karancin abunda ake bukata domin cin gajiyar shirin.