BUHARI DA ASUU
Takun sakar dake tsakanin kugiyar malaman Jami’oi ta kasa ASUU da kuma gwamnatin taraiyya ka iya kara dagulewa, biyo bayan yadda Ma’aikatar Ilimi ta kasa ta baiyana cewa yarjejeniyar dake tsakaninta da kungiyar Malaman jami’oi ta kasa, ba zata yi aiki akan jami’oin jihohi ba.
Wani kwamiti da gwamnatin taraiyya ta kafa a karkashin uban jami’ar Lokoja, Farfesa Nimi Briggs , Ya bada shawarar biyan malaman jami’oin akan karin kaso 180 bisa 100, to amma gwamnatin taraiyya tace zata yi karin kaso 100 bisa 100 ne kawai.
Kazalika Kakakin Ma’aikatar Ilimi ta kasa, Ben Goong a wata hira da aka yi dashi jiya Abuja, Ya baiyana cewa gwamnatin taraiyya ba zata tsoma bakinta kan harkokin da suka shafi tafiyar da ilimi a matakan jihohi, kasancewar yana a bangaren kebantattun abubuwa da doka ta tsara.
A martaninsa shugaban Kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Osodoke , Yace dole ne duk wata yarjejeniya da suka kulla tsakaninsu da gwamnatin taraiyya ta shafi jami’oin jihohin.
A yanzu dai a iya cewa a yanzu an bude wani sabon babin takaddama tsakanin gwamnatin taraiyya da kuma kungiyar ASUU.
More from Labarai
-
An Hana Gidajen Talabijin Na Kasar Kenya Gabatar Da Sakamakon Zaben Shugaban Kasa
A yayin da ake cigaba da kidaya kuri’ar zaben shugaban kasa a kasar Kenya wanda aka yi a ranar Talata, A yanzu haka an hana gidajen Talabijin na kasar cigaba da gabatar da sakamakon zaben kai tsaye.
-
Jigon Rahoton Mu Na Wannan Mako Akan Ambaliyar Ruwa Da Ta Addabi Wasu Sassan Kano
Audio
Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya na sa'o'i 48 da aka samu a wasu sassan jihar nan, a ranakun 2 da 3 ga watan Agusta, sai dai ya jawo gagarumar asara, data hada da asarar rayuka da dumbin dukiyoyi na miliyoyin naira.
-
An samu Raguwar Masu Aikata Lefuka Da Babur Din Adaidaita Sahu A Kano
Shugaban Hukumar KAROTA, Baffa Babba Dan’agundi, Yace dokar takaita zirga-zirgar Babura masu kafa ukku daga karfe 10 na dare zuwa washewar gari, ta haifar da ‘Da mai Ido.
-
Gwamnoni Sun Zargi Ministan Shari'a Da Arzuta Kansa Da Kudaden Paris Club
Kungiyar gwamnonin kasar nan ta mayar da martani ga babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a Abubakar Malami SAN, bisa takaddamar wasu kudade kimanin dala miliyan 418, na kudaden Paris Club da aka dawo da su.
-
Gwamna Wike Yace Masu Hamaiyya Dashi Zasu Sha Mamaki Gabanin Zabe Mai Zuwa
Gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike yayi alkawarin kara rubunya harkokokin siyasarsa daga jiharsa gabanin babban zaben kasar nan mai zuwa, inda ya baiyana cewa dabarun da zai yi amfani zasu bawa abokan hamaiyyarsa mamaki.