On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Hukumar Zabe Ta Turo Sabon Kwamishinan Zabe Na Jihar Kano

FARFESA MAHMOOD YAKUBU SHUGABAN HUKUMAR ZABE TA KASA

Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta, ta turo Ambassador Abdu Abdussamad Zango, a matsayin sabon kwamishinan zabe na jihar Kano.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci bukin rantsawar  a ranar Alhamis a shalkwatar  Hukumar INEC da ke Abuja, ya gargade su dasu guji kai yawan ziyara gidajen gwamnatocin jihohin da aka tura su, domin kare mutuncinsu.
Idan dai ba  a manta ba a watan Yuli ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sunayen mutane 19 da aka nada a matsayin kwamishinoni a hukumar  INEC ga majalisar dattawa domin tantancewa.