On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ta Umarci Malaman Jami'ar Jihar Dasu Koma Bakin Aiki

TAMBARIN JAMI'AR UMARU MUSA YAR ADUWA

Majalisar dokokin jihar Katsina ta bawa kungiyar malaman jami’o’I ta kasa ASUU, reshen jami’ar , Umaru Musa Yar’adua, wa’adin makonni 3 kan su dawo cigaba da aiki a ranar 5 ga watan Satumba.

Shugaban kwamitin ilimi mai zurfi  wanda ke wakiltar mazabar Danja, Alhaji Shamsudeen Da'bai, shine ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a birnin jihar.

Ya bayyana cewa, gazawar malaman ta komawa aiki cikin karshen wa’adin mako 3, majalisar zata bawa gwamnatin jihar umarni, kan ta dakatar da albashin su.