Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA a jihar ta tabbatar...
Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana mummunar fashewar da ta afku a haramtaciyar matatar mai dake jihar Imo amatsayin wani bala'i na ƙasa baki daya, yana mai cewa Najeriya na cikin kaɗuwa da tashin hankali.
A cikin wata sanarwa da mai magan da yawunsa Mallam Garba Shehu ya fitar, shugaban kasar ya umarci hukumomin tsaro na soji da jami’an leken Asiri da su kara azama wajen gudanar da ayyukan kakkabe haramtattun matatun man Fetur dake sassan kasarnan..
Buhari yace wajibi ne a dora alhakin asarar rayuka da dukiyoyi sanadiyar Iftila’in akan wadanda suke daukar nauyi ko gudanar da haramtattun matatun mai, wanda ya ce dole ne a kama su baki daya kuma su fuskanci hukunci.
Ya kuma bukaci shugabannin al’umma da ‘yan sanda da masu kula da bayanan sirri su kare afkuwar irin hakan a nan gaba..
A wani bangaren kuwa, yawan mutanen da suka gamu da ajalinsu sanadiyar gobarar ya karu zuwa 110..
Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA a jihar ta tabbatar da cewa an samu karuwar mutum 1 a cikin yawan mutanen da suka mutu zuwa 110.
Shugaban sashen gudanarwa na hukumar bada agajin gaggawa NEMA Mr Ifeanyi Nnaji, yace karin mutum dayan da aka samu wata mat ace mai dauke da juna biyu.
More from Labarai
-
An Hana Gidajen Talabijin Na Kasar Kenya Gabatar Da Sakamakon Zaben Shugaban Kasa
A yayin da ake cigaba da kidaya kuri’ar zaben shugaban kasa a kasar Kenya wanda aka yi a ranar Talata, A yanzu haka an hana gidajen Talabijin na kasar cigaba da gabatar da sakamakon zaben kai tsaye.
-
Jigon Rahoton Mu Na Wannan Mako Akan Ambaliyar Ruwa Da Ta Addabi Wasu Sassan Kano
Audio
Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya na sa'o'i 48 da aka samu a wasu sassan jihar nan, a ranakun 2 da 3 ga watan Agusta, sai dai ya jawo gagarumar asara, data hada da asarar rayuka da dumbin dukiyoyi na miliyoyin naira.
-
An samu Raguwar Masu Aikata Lefuka Da Babur Din Adaidaita Sahu A Kano
Shugaban Hukumar KAROTA, Baffa Babba Dan’agundi, Yace dokar takaita zirga-zirgar Babura masu kafa ukku daga karfe 10 na dare zuwa washewar gari, ta haifar da ‘Da mai Ido.
-
Gwamnoni Sun Zargi Ministan Shari'a Da Arzuta Kansa Da Kudaden Paris Club
Kungiyar gwamnonin kasar nan ta mayar da martani ga babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a Abubakar Malami SAN, bisa takaddamar wasu kudade kimanin dala miliyan 418, na kudaden Paris Club da aka dawo da su.
-
Gwamna Wike Yace Masu Hamaiyya Dashi Zasu Sha Mamaki Gabanin Zabe Mai Zuwa
Gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike yayi alkawarin kara rubunya harkokokin siyasarsa daga jiharsa gabanin babban zaben kasar nan mai zuwa, inda ya baiyana cewa dabarun da zai yi amfani zasu bawa abokan hamaiyyarsa mamaki.