On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Mutane Dubu 70 Ne Suka Nemi Aikin Koyarwa A Jihar Kaduna

GWAMNA EL-RUFA'I NA JIHAR KADUNA

Hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar Kaduna ta tabbatar da cewa mutane akalla dubu 73 ne suka nemi aikin koyarwa a makarantun firamare wanda a baya hukumar ta sanar zata dauki mutane dubu 10.

Shugaban hukumar Alhaji Tijjani Abdullahi ne ya bayyana hakan a yau, a lokacin da aka fara rubuta jarabawa ta hanyar amfani da na’ura mai kwakwalwa ga wasu daga cikin mutanen da aka zaba daga cikin masu neman aikin a jami’ar jihar Kaduna.

Abdullahi wanda Mubarak Mohammed jami’in hukumar ya wakilta, yace ana gudanar da jarabawar ne bi da bi a cibiyoyi dake Kaduna da Zaria da Kafanchan.

Yace jarabawar wadda aka fara a ranar 17 zuwa 28 ga watan nan da muke ciki, za’a yita ne cikin tsanaki, yana mai cewa mutane masu kwazo kuma wadanda suka cancanta ne kawai za’a dauka aikin.

More from Labarai