On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Abba Gida-Gida Ya Zargi Shugabannin kananan Hukumomin Jihar Kano Da Fitar Da Wasu Makudan Kudi Domin Gudanar Zabukan Cike Gibi A Nan Jihar Kano

ABBA GIDA-GIDA

Zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf Ya gargadi shugabannin kananan hukumomi da kuma manyan jami’an gudanar da mulki na kananan hukumomin dasu guji yin amfani da wasu makudan kudade da aka ware da sunan gudanar da zabukan cike gibi da za’a gudanar a wasu wurare a gobe Asabar.

A cikin wata sanarwa  ta shawara  da zababben gwamnan na kano, Abba Gida Gida  ya fitar ta hannun  kakakinsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa , wanda  ya baiyana cewar sun samu cikakkun bayanai  kan  yin amfani da kudaden.

Ya yi zargin cewar  gwamnatin jihar Kano  ta bada umarnin sakin sama da naira milyan sittin-sittin ga kananan hukumomin Doguwa da Nasarawa da Wudilm  yayin da wasu kananan hukumomin zasu karbi daruruwan dubunan kudade da sunan  gudanar da zaben  cike  gibin

To sai dai duk da kasancewar  har ya zuwa wannan lokaci gwamnatin jihar Kano bata  mayar da martani akan wannan sabon zargi  da gwamnati mai jiran gado ta  yi  ba, Sai dai idan ba’a manta ba, A makon jiya ne  kungiyar shugabannin kananan hukumomi ta jihar Kano ALGON ta kalubalanci  gwamnati mai jiran gado, inda ta zarge ta  da dumama  yanayin da ake ciki.

Sanarwar  mai dauke dasa hannun  shugaban kungiyar  Shugabannin kananan hukumomi a nan jihar Kano Baffa  Mohammed, Ya musanta zarge-zargen da  zababben gwamnan  jihar Kanon ya yi,  na  tuhumar  shugabannin kananan  hukumomi  da karya  dokokin tafiyar da kudi.

Ya kara da cewar  ba sabon abu bane  a rikin samun irin wannan zargi da bashi da tushe balle makama  a duk lokacin  da aka samu sabuwar  gwamnati.