On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Amurika Zata Dafawa Tinubu Baya Domin Inganta Tattalin Arziki Da Tsaro

Shugaban kasar Amurika,Joe Biden ya yi alkawarin yin aiki tare da sabon shugaban kasa, Bola Tinubu ta fannin inganta tattalin arziki da kuma sha’anin tsaro.

Shugaba Joe Biden wanda ya turo tawaga mai karfi daga Amurika domin shaidar bukin rantsar da Tinubu, ya baiyana haka ne ta cikin wata sanarwa, wadda ke  taya  Tinubun murnar rantsuwar kama aiki da  yayi a ranar litinin.

Ya  jaddada  kudirin gwamnatinsa  na yin aiki kafada da kafada  da  Tinubu domin karfafa  zumuncin dake  tsakanin Amurika da kuma  nan Najeriya.

Joe Biden  ya  ce  yana da kwarin gwiwa akan  irin ingantattun   manufofi dake tsakanin kasashen biyu.