On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

An Bukaci Kotu Ta Hana Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Kasa

TINUBU

Tsohon Dan Takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2019, Ambrose Owuru, Ya garzaya gaban kotun daukaka kara dake Abuja domin ganin an hana rantsar da zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a matsayin sabon shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayun bana.

Owuru wanda ya  nemi takarar a karkashin rusasshiyar jam’iyyar HDP, Ya bukaci kotun daukaka karar  data hana  ministan shari’a na kasa, Abubakar Malami da hukumar zabe ta kasa  rantsar da Tinubu a matsayin sabon shugaban taraiyyar kasar nan.

Ambrose  ya yi ikirarin shi ne wanda ya samu nasara a zaben shekarar  2019,kuma har yanzu  wa’adin mulkinsa  bai kare ba,kasancewar kotun  koli  har yanzu bata yanke hukunci kan karar  da ya shigar gabanta ba, inda yake kalubalantar aiyana Buhari a matsayin wanda ya lashe  zaben shugaban kasa a wannan lokaci.

Kunshin takardar karar na dauke ne da sadarori  har guda takwas,inda  kuma yayi fatan za’a saurareta  kafin ranar 29 ga watan gobe, To sai dai kuma kotun bata saka lokacin da zata  fara zaman shari’ar ba.