On Air Now

Off Air

Midnight - Noon

An Fara Saka Kyamarorin Tsaro A Jiragen Kasa

JIRAGEN KASA

Biyo bayan sauyin lokacin da za’a dawo zirga-zirgar jiragen kasa daga Abuja zuwa Kaduna, A yanzu haka gwamnatin taraiya ta fara saka kyamarorin tsaro a dukkanin taragun dake cikin jiragen kasar.

Hakan na zuwa ne yan kwanaki bayan da ministan sufuri, Mu’azu Sambo  ya bada sanarwar  dage lokacin da za’a dawo da zirga-zirgar jiragen kasar.

A jiya ne  ‘yan kwangilar da aka baiwa aikin, suka  fara saka kyamarorin tsaron a tashar jirgin kasa ta Idu dake Abuja.

Kakakin Hukumar Kula da Sufurin jiragen kasa ta Najeriya Mahmood Yakubu, Yaki cewa tak kan matakin lokacin da ake nemi jin ta bakinsa.