On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

An Kama Tsohon Kwamishinan Ayyuka A Kano Da Wasu Mutum 5 Bisa Zargin Badakalar Sama da Billiyan 1

Hukumar karbar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano ta kama tare da tsare, Injiniya  Idris Wada Saleh kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, da wasu mutane biyar bisa zargin almundahanar Naira biliyan 1.

Rahotanni sun bayyana cewa an kama Saleh, wanda kuma shi ne tsohon shugaban hukumar kula da gyaran Tituna Kano a ranar Litinin da yamma tare da babban sakatare na ofishin kula da bada kwangilolin gwamnati, Mustapha Madaki da  Daraktan kudi da daraktan bincike da tsare-tsare tare da wasu sauran mutane.

An kama su ne bisa zargin fitar da sama da Naira biliyan 1 domin gyaran tituna 30 da magudanar ruwa a cikin  birnin Kano da ba a aiwatar ayyukan  ba.

Wata majiya a hukumar ta yi nuni da cewa an biya kudaden da aka  kashi uku ne a asusun kamfanoni uku a ranar 25 ga watan Afrilu na 2023.

Kakakin hukumar Abba Kabir ya ce wadanda aka kama suna fuskantar tambayoyi kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.