On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

An Kubutar Da Mutane 8 Da Ake Yunkurin Fataucinsu Zuwa Kasashen Ketare A Jihar Jigawa

Hukumar kula da shige da fice ta kasa ta ceto wasu mutane takwas da ake yunkurin  safararsu a  jihar Jigawa.

Kwanturolan hukumar reshen jihar Jigawa, Ahmad Dauda Bagari  shine ya tabbatar wa manema labarai hakan  ofishinsa dake Dutse babban birnin jihar.

Ya ce jami’an hukumar  ne suka kama wadanda al’amarin ya rutsa da su a ranar Lahadi a kan hanyarsu ta tsallakawa Jamhuriyar Nijar a karamar hukumar Roni.

Wadanda aka kubutar  sun hada da maza biyar da mata uku daga jihohi hudu na Abia da  Edo da  Imo da kuma Ogun, kuma shekarunsu na  tsakanin  19 zuwa 45, ba su da ingantattun takaddun balaguro.

Bagari, Yace mutanen suna tafiya ba tare da wakili ba, inda suke yin duk ma'amalarsu   ta waya, sai dai ya nunar da  cewa babu wani abu da aka samu na laifi ko kwaya a hannunsu.

Nigeria Immigration Service

An bada umarnin mika mutanen ga hukumar NAPTIP sannan kuma ya shawarci iyaye da ‘yan uwa da sauran jama’a da su daina yarda suna tura ‘ya’yansu zuwa kasashen waje kasancewar Najeriya tana da yanayi mai kyau na rayuwa mai inganci tare da sanya kishin kasarsu ta asali da kuma gina ta zuwa ga kololuwar mataki.

Haka kuma hukumar ta kara shawartar jama’a da su sauke  nauyin da ya rataya a wuyansu ta hanyar kai rahoton laifukan safarar mutane da sauran laifuffuka masu alaka da su ga hukumomin tsaro mafi kusa.