Tsofaffin sojojin Najeriya sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta fara aiwatar da mafi ƙarancin albashin naira dubu 250 da aka amince da shi ga jami'an sojin da ke aiki.
Sun bayyana hakan ne yayin wani taron bitar da suka gudanar a Abuja, inda suka ce Majalisar Dokoki ta amince da sabon tsarin albashin, kuma Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu a dokar, sai dai har yanzu ba a fara aiwatar da ita ba.
Tsofaffin sojojin sun bayyana rashin jin daɗinsu kan jinkirin, suna mai cewa an yi wannan gyaran albashi ne bayan wani bincike ya bayyana cewa sojojin Najeriya na daga cikin waɗanda ke karɓar mafi ƙarancin albashi a nahiyar Afirka.
Comments
Add a comment