On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

An Tantance Alkalai 11 Domin Zama Sabbin Alkalan Kotun Kolin Najeriya

Majalisar koli kan harkokin shari'a ta kasa NJC ta bada shawarar anada alkalai 11 amatsayin Alkalan kotun koli.

Sanarwar da Daraktan Yada Labarai na majalissar, Soji Oye ya fitar a ranar Laraba, ta ce an cimma matsayar ne a karshen zaman majalisar na 104.

Kundin tsarin mulkin kasarnan ya tanadi alkalai 21 a kotun koli amma a halin yanzu kotun tana da alkalai 10 mafi karanci a tarihi.

Hukumar NJC ta tantance ‘yan takarar zama Alkalan kotun koli 22 da hukumar kula da harkokin shari’a ta tarayya ta tantance, kuma a ranar Laraba ta zabi sunayen mutum 11 da suka yi nasara a shafinta na intanet.

Ana sa ran hukumar ta NJC za ta mika sunayen ga shugaban kasa domin amincewa da su kafin ranar Juma’a.