On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

An Tura Jami'an Tsaro Sassan Abuja Da Kaduna Domin Kulawa Da Sufurin Jirgin Kasa A Najeriya

Babban Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya  Usman Baba, ya bayar da umarnin tura jami’an tsaro da za su bada kulawa da matafiya a  titin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna, yayin da a yau litinin ake dawowa  cigaba da jigilar Fasinjoji bayan kusan wata tara da dakatarwa sanadiyar harin ‘yan ta’adda.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, a wata sanarwa da ya fitar a karshen mako, ya ce za a zabo jami’an ne daga wata rundunar ‘yan sanda da ake kira K-9 da ofishin leken asiri na rundunar ‘yan sandan da sashen kwance abubuwan fashewa da sauran makamantansu.

Adejobi ya ce rundunar ‘yan sandan Najeriya na tattaunawa akai-akai da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa da sauran jami’an tsaro a shirye-shiryen dawowa aiki a yau.

Ya ce babban Sifetan ya baiwa jama’a, musamman ma fasinjoji tabbacin kulawa da  rayuka da dukiyoyinsu.