On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

An Wayi Gari Da Durkushewar Lantarki A Najeriya

Babban layin wutar lantarki na kasa karkashin kulawar  kamfanin tura wutan lantarki na kasa TCN ya lalace da tsakar daren  yau  Alhamis, al'amarin da ya jefa Najeriya cikin duhu  baki ɗaya.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa durkushewar  na zuwa ne makonni kadan bayan da kamfanin tura wutar lantarki na kasa TCN ya yi bikin shafe sama da shekara guda ba tare da  samun durƙushewar wutar lantarki a Najeriya ba.

Wata sanarwar da kamfanin Rarraba  Lantarki na  Enugu (EEDC) ya fitar, ya ce ɗurƙushewar ta afku ne da karfe 12:40 dare  s wanda ya yi sanadin daukewar wuta a faɗin ƙasar.

Sanarwar ta ce saboda wannan matsala ta durƙushewar layin wutar lantarki a Nageriya, duk tashoshin TCN ba su da wadatar turawa abokan hulda  hakan yasa ba za'a  iya tura wuta ga  jihohin Abia da Anambra da Ebonyi da Enugu da kuma Imo ba.