On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Ana Tsaka Da Shan Suka Gwamnatin Najeriya Ta Bayyana Adadin Wakilanta A Taron COP28 Na Dubai

Gwamnatin Tarayya ta ce ta dauki nauyin wakilai 422 ne kawai daga cikin ‘yan Najeriya dubu 1 da 411 da aka rawaito suna halartar taron sauyin yanayi na COP28 da ke gudana a Dubai.

Wannan bayanin dai na zuwa ne bayan fusatar da ‘yan Najeriya suka  nuna kan yawan tawaga da suka halarci taron, duk da karuwar fatara da yunwa da ake fusknata  fadin kasarnan.

Da yake mayar da martani a cikin wata sanarwa a ranar Litinin, Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya ce an zabo wakilai 422 daga fadar shugaban kasa da  majalisar kasa kan sauyin yanayi da dukkan ma’aikatu da  ofishin mataimakin shugaban kasa da  majalisar dokoki ta kasa, da hukumomin tarayya.

Ya ce, a matsayinta na kasa mafi karfin tattalin arziki kuma mafi yawan al’umma a Afirka, da ke da matukar hadari ga sauyin yanayi, Najeriya na da muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manufofin taron, don haka shigar da masu ruwa da tsaki  babban taron na duniya ya zama dole.