On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

ASUU Ta Koka Kan Kara Kudin Makaranta

OSODOKE

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bukaci gwamnatin tarayya ta sake duba kan karin kudin makaranta da ake samu yanzu haka a makarantun Hadaka na kasar nan.

Ya bukaci gwamnati da ta yi abunda da ce  domin  samarwa  matasa  wanda sune  shugabannin kasar nan  a gobe, mafita wajen gudanar da karatunsu.

Osodeke ya kalubalanci  matakin kara  kudin makarantar da aka yi a makarantun Hadaka  na kasar nan da  kuma manyan makarantun da ake dasu.

Ya fadawa manema labarai cewa karin kudin zai yi babbar  illa ga makomar karatu a kasar nan.