On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Bani Da Masaniya Kan Billiyan 206 A Kasafin Kudin Ma'aikatar Jin Kai - Sadiya Faruk

Kwamitin ayyuka na musamman na majalisar dattawa ya gayyaci ministar kudi da kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmed kan sanya kudi naira biliyan 206 a cikin kasafin kudin shekarar 2023 na ma’aikatar jin kai.

Shugaban kwamitin Sanata. Yusuf Yusuf shine ya sanar da hakan  a lokacin da ministar harkokin jin kai, Sadiya Farouq, ta bayyana gaban kwamitin a ranar Litinin domin kare kasafin.

An tambayi ministar akan kimanin Naira biliyan 206 a cikin kasafin kudin da ta yi niyyar ciyo bashi. Nan take ta ba da amsar cewa an gabatar da irin wannan adadi a kasafin kudin shekarar 2022 amma ba a saki kudaden ba.

Sai dai ta musanta masaniya game da yadda adadin  ya sake kunno kai a cikin kasafin kudin shekarar 2023 da ake shirin yi, al’amarin da ya sa kwamitin ya gayyaci ministar kudi domin amsa tambayoyi.