On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Dalibai Za Suyi Zanga-Zangar Adawa Da Karin Kudin Makaranta

DALIBAI

A yaune Kungiyar Dalibai ta kasa zata gudanar da zanga-zanga domin nuna adawarta da karin kudin makaranta da aka yi a manyan makarantun kasar nan.

Kungiyar ta kudiri cewar  ‘ya’yanta zasu yi  zanga-zangar a jami’ar  Legas, tare da gargadin  jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS  da kada su hana daliban ‘yancinsu  na  yin zanga-zangar.

Kakakin kungiyar  Giwa  Temitope ne ya baiyana haka lokacin da yake mayar da martani kan sanarwar da hukumar DSS ta fitar,  Wanda  ta baiyana cewar wasu ‘yan siyasa  sun dauki  nauyin dalibai domin yin zanga-zanga akan gwamnatin taraiyya dangane da halin da kasa ke ciki.

Sai dai ya fadawa manema Labarai  cewar  zanga-zangar su ta neman yanci ne a kokarinsu na ganin  an  janye  karin kudin makaranta da aka  yiwa  daliban.