On Air Now

Off Air

Noon - 6:00pm

Daya Daga Cikin Motocin Da Ta Dauki 'Yan Najeriyar Da Suka Makale A Sudan Ta Kama Da Wuta

‘Daya daga cikin motocin safar dake dauke da ‘Yan Najeriyar da suka makale a kasar Sudan wadda take kan hanyar zuwa Birnin Port Sudan dake bakin gabar tekun kasar, domin tsallakar dasu zuwa kasar Saudiyya a jiya ta kama da wuta.

Sama da  ‘yan Najeriya dubu ne aka kwashe  ta hanyar amfani da birnin na Port  Sudan, biyo bayan tsauraran sharudda  da rukunin farkon na  ‘yan Najeriya  da aka kwashe ke fuskanta  akan iyakokin kasar  Masar.

Rahotanni sun baiyana cewar  Motocin safa  26 ne  suka sauki  ‘Yan Najeriyar  da suka makale a kasar  daga  Al-Razi  da karfe  12 na daren  jiya  zuwa  gabar  tekun kasar, Sai dai daya  daga cikin motocin dake  dauke da mutane 50 ta lalace  sakamakon tsananin zafi  da  ya yiwa  daya daga cikin tayoyin motar yawa.

Daga cikin mutanen dake cikin motar  mai suna  Sani Aliyu ya tabbatar da  faruwar lamarin, ya  ce  an  rarraba mutane  40  daga cikin  50 dake  cikin motar  zuwa  cikin sauran motocin Safar, A  yayin da ragowar Goman kuma suka  shafe  daren jiya a wajen  da abun ya  faru.

Rahotanni sun baiyana  cewar  daga bisani  ‘yan Najeriya sun cigaba da  balaguron zuwa  gabar   birnin.

A yanzu haka dai akwai ‘yan Najeriya masu yawan gaske da suka shafe kimanin kwanaki biyar akan iyakokin kasar Masar,  a yayin da jami’an kasar  suka hana su  shiga  cikin Masar  wanda  ta nan  ne  jirage  zasu dauko su zuwa Najeriya.