On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Emefiele Ya Musnta Zargin Rahoton Mai Bincike Na Musamman Kan CBN

Tsohon gwamnan babban bankin kasa CBN Emefiele, ya musanta rahoton da babban mai bincike na babban bankin, Jim Obazee, ya bayar na cewa ya ajiye kudi fam milliyan 543 da dubu 482 da 213 a bankunan kasar Birtaniya da sauran su ba tare da izini ba.

Emefiele, wanda aka saki daga gidan yarin na Kuje a karshen mako, ya bayyana hakan ne a daren jiya a cikin wata sanarwa, inda ya bayyana rahoton a matsayin yaudara da kuma kididdigar kokarin da ake yi na cutar da shi da kuma biyan bukatar son kai ta mai binciken.

Ya ce sassan da abin ya shafa na CBN suna da hurumin gudanar da irin wadannan ayyuka kamar yadda doka ta tanada a cikin CBN.

Emefiele ya nunar da cewa ya umarci lauyoyinsa da su fara aikin shari'a don wanke sunansa daga maganganun batanci da ke kunshe a cikin rahoton.