On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Ganduje Na Fuskantar Kalubale Kan Zama Shugaban Jam'iyyar APC

GANDUJE

Yunkurin ganin Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa, na cigaba da fuskantar babban kalubale, A yayin da mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa mai kula da shiyyar Arewa maso yamma, Salihu Lukman, ya kalubalanci matakin, inda ya baiyana cewar yankin Arewa ta tsakiya ce ya kamata ta cigaba da rike kujerar shugabancin jam’iyyar, tare da yin kira ga shugaban kasa Bola Tinubu akan ya kyale kwamitin gudanarwar jam’iyyar ya zabi wanda zai gaje buzun tsohon shugaban jam’iyyar APCN na kasa, Sanata Abdullahi Adamu.

Wata majiya  ta baiyana cewar  Ganduje  ya yi wata ganawar sirri  da sakataren gwamnatin taraiyya, George Akume  jiya a Abuja, A cigaba da fadi tashin  da  yake  na ganin  ya  dare kan shugabancin jam’iyyar na kasa.

To sai  dai yankin Arewa ta tsakiya  na cigaba da matsa lamba kan cewar, inda za’a yi adalci  da kamanta gaskiya,  kamata  ya yi  kujerar  ta cigaba da kasancewa a hannunsu,  kasancewar  it ace  yankin da aka zaba  domin  shugabancin jam’iyyar, a babban taron jam’iyyar da aka yi a bara.