On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Ganduje Ya Bukaci Kotu Ta Hana EFCC Yi Masa Bincike Kan Faifan Bidiyon Dala

Tsohon gwamnan jihar Kano,Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci babbar kotun taraiyya dake zamanta a nan Kano, Da ta hana hukumar EFCC yi masa bincike kan wani faifan bidiyo da aka ga tsohon gwamnan yana karbar Daloli daga hannun wani ‘Dan kwangila, a matsayin cin hanci.

A cikin kunshin karar da tsohon gwamnan ya shigar da hukumar EFCC,  Ya nemi kotun  da  ta yi  la’akari da karfin da kundin  tsarin  mulkin kasa  ya baiyana,  wanda ya nuna cewar  hukumar ta EFCC  bata  da ikon  binciken tsohon gwamna,  kasancewar maganar  tana a gaban zauren majalisar dokokin jihar Kano.

Karar  wadda tsohon babban lauyan gwamnatin kano, M A Lawan ya shigar gaban kotun,  Ya nemi  kotun ta tilastawa  hukumar  EFCC janye  gaiyyatar da ta yiwa  shugaban hukumar ilimin bai daya  da  kuma daraktan kudi  na hukumar  tare da  babban akanta  na jihar kano,   domin yi masu bincike kan  abunda keda  alaka  da  faifan bidiyon karbar dalar.

Lauyan Ganduje  ya  ce  kamata  ya yi hukumar  ta bari a kammala  shari’ar  dake tsakanin tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje da kuma mawallafin jaridar  Daily Nigeria Ja’afar Ja’afar dake  gaban wata babbar  kotun taraiyya a Abuja, kafin daukar wani mataki a kai.