On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Gwamna Dare Ya Rage Yawan Ma'aikatu Da Hukumomin Gwamnati A Jihar Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umurnin rage yawan ma’aikatu daga 28 zuwa 16 a ranar Alhamis.

Lawal ya ce an dauki matakin ne don sauya fasalin aikin gwamnati da nufin  samar da Nagartar da ake bukata a jihar.

Gwamnan ya sanar da matakin ne a kafafen sada zumunta na zamani, inda ya ce ya yi dai-dai da manufarsa na samar da majalisar zartaswa  mai aiki da zata rage tsadar tafiyar da mulki da samar da ribar dimokuradiyya.