On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Gwamna Ortom Na Jihar Benuwe Ya Rubutawa Shugaba Buhari Wasikar Neman Izinin Mallakar Makamai Ga Sabbin Jami'an Tsaron Sa Kai.

Gwamna Samuel Ortom na jihar Benuwe ya rubutawa shugaban kasa Muhammadu Buhari wasikar neman lasisin mallakar bindigogi ga sabbin jami’an sa kai na jihar Binuwai da aka kaddamar a makon jiya.

Ortom wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin a Makurdi, yace matakin ya zama dole ne biyo bayan halaltacciyar  hanyar da akabi wajen kafa jami’an tsaron na sa kai don taimakawa wajen dawo da zaman lafiya a sassan jihar da ke fama da rikici. 

Ya ci gaba da cewa yana fatan shugaban kasa zai amince da bukatarsa ​​ta karfafawa  ‘yan kasa don tabbatar da matakin kare kai. 

A yayin kaddamar da jami'an a makon da ya gabata, Gwamnan ya bukaci jami'an da su guji yin amfani da karfin ikon da dokar jihar ta ba su wajen wuce makadi da rawa.