Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada matsayinta na nuna halin ba sani ba sabo kan yaki da da cin hanci da rashawa a dukkanin hukumomi da ma'aikatun gwamnati, tana mai nanata aniyarta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a bangaren gudanar da aiyukan gwamnati.
An sake bayyana wannan matsaya ne a wani taron bitar samun ƙwarewa da ka shiryawa sabbin manyan sakatarori 19 da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa a baya-bayan nan domin su yi aiki a hukumomi daban daban.
Da yake jawabi ga mahalarta bitar da ke gudana a Kaduna, Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, Comrade Sa'id Yahya, ya ce taron na daga cikin matakan da ake ɗauka domin ƙarfafa ɗabi'ar gaskiya da dakile ayyukan rashawa a ɓangaren gwamnati.
A cikin saƙon murya da ya aikowa Arewa Radio ta manhajar WhatsApp, Comrade Sa'id Yahya ya ce hukumar na ci gaba da samun nasara.
Comments
Add a comment