On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Gwamnatin Taraiyya Na Kashe Sama Da Naira Bilyan 18 A Kowace Rana Domin Biyan Tallafin Mai

MINISTAR KUDI

Ministar Kudi, Hajiya Zainab Ahmed Shamsuna tayi kiyasin cewa Najeriya na kashe naira Bilyan 18 da Milyan 39 a kowace rana domin biyan kudin Tallafin Mai.

Ministar  ta baiyana haka ne a yayin  zaman jin ba’asi da  kwamitin wucin gadi na zauren  majalisar wakilai  ya shirya, domin jin yadda  gwamnati ta biya kudaden  tallafin mai daga shekarar  2017 zuwa  2021.

A cewarta an gano yawan kudaden ne a bisa bayanan  lissafin da Kanfanin Mai na kasa  da hukumomin da abun ya shafa  suka bayar.

Ministar Kudin ta kara da cewa, Bayanai sun nuna cewa ana  amfani da  Lita Milyan 64 da Dubu 96 a kowace rana a kasar nan, A yayin da aka biya naira tiriliyan Daya da Bilyan 774 ga Dillalan mai masu zaman kansu a matsayin kudaden Tallafin Mai a cikin shekaru 4 da suka gabata.

 

A nan kuma Kwamitin wucin gadi na zauren majalisar wakilai da aka kafa domin yin bincike kan yadda gwamnatin taraiyya  take biyan kudaden tallafin mai tun daga shekarar  2013 zuwa 2022,Ya tuhumi ministan kudi Kasafi da kuma tsare-tsaren cigaban kasa, Zainab Ahmed kan yadda gwamnatin taraiyya ke biyan kudaden tallafin mai.

A jawabinta, Ministar ta baiyana  cewa gwamnatin taraiyya ba zata iya cigaba da biyan kudaden tallafin mai ba, kasancewar  biyan kudaden ka iya sawa gwamnati ta fi yawan ciwo bashi.

Tace a yanzu gwamnatin taraiyya tayi tanadin biyan tallafin mai ne zuwa rabin shekara mai kamawa kadai, kamar yadda yake kunshe cikin daftarin kundin tsare-tsaren kasafin kudi na shekarar  2023 zuwa 2025.