On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Gwamnatin Taraiyya Ta Amince Da Jinginar Da Filayen Jiragen Sama Na Kano Da Abuja

FLININ JIRGIN SAMAN MALAM AMINU KANO

Majalisar zartarwa na kasa karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta amince da jinginar da filayen sauka da tashin jiragen sama Nnamdi Azikwe dake Abuja da kuma filin jirgin sama Mallam Aminu Kano dake nan nan Kano.

Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Wanda  ya  tabbatar da haka, ya ce za a  jinginar  da  filin saman Abuja  na tsawon shekaru 20, yayin da na Kano zai dauki  tsawon shekaru 30 a matsayin jingina.

Hadi  Sirika ya  kuma baiyana cewar  majalisar ta kuma amince da sauya sunan ma’aikatarsa daga ma’aikatar sufurin jiragen sama ta kasa   zuwa ma’aikatar sufurin jiragen sama da  kula da  sararin samaniya ta kasa.

Ya ce majalisar ta kuma amince da daftarin manufofin zirga-zirgar jiragen sama na kasa da duniya ke amfani dasu a halin yanzu.