On Air Now

ZANGON RANAR ASABAR

Noon - 6:00pm

Gwamnatin Taraiyya Ta Bukaci Kotun Koli Ta Kori Karar Neman Tsawaita Wa'adin Yin Amfani Da Tsaffin Kudi

MALAMI

Gwamnatin taraiyya ta bukaci Kotun Koli data kori karar da aka shigar gabanta wadda ake neman a dakatar da gwamnatin taraiyya daukar matakin hana yin amfani da tsaffin kudi daga ranar 10 ga watan da muke ciki.

Idan  ba’a manta ba,Babban bankin kasa  ya fara  saka  wa’adin ranar   31  ga watan janairu  a matsayin lokacin  da  za’a  dena  yin amfani  da tsaffin takardun kudin  kafin daga  bisani  ya  tsawaita  zuwa  10  ga watan   Fabarairun da muke  ciki.

A  hukuncin da kotun kolin ta yanke  a  jiya  karkashin   Alkalai  guda  bakwai,bisa  jagorancin  mai shari’a John Okoro , ta dakatar  da gwamnatin  taraiyya daga daukar  matakin hana  yin amfani da tsaffin kudin ,  biyo  bayan karar  da  gwamnatocin jihohin Zamfara  da Kogi da kuma Kaduna  suka shigar  gabanta.

To  sai  dai a  bukatar  da   gwamnatin taraiyya ta shigar  gaban kotun,ta hannun babban lauyan gwamnatin taraiyya, Ta  baiyana  cewa Kotun kolin bata da  hurumin  sauraren shari’ar , sannan kuma masu kara  basu  gabatar da wasu kwararan  hujjoji  akan  matakin da suka dauka.

Daga  bisani  kotun kolin  ta dage  zamanta zuwa ranar  15  ga watan   Fabarairu  da muke ciki.