On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Gwamnatin Taraiyya Ta Fitar Da Naira Milyan 150 Domin Hayar Motocin Da Zasu Kwashe 'Yan Najeriya A Sudan

SUDAN

A yaune gwamnatin taraiyya zata fara aikin kwashe ‘Yan Najeriyar da suka makale a Khartoum babban birnin kasar Sudan, da sauran wasu birane na kasar , su kimanin dubu 5 da 500 ,biyo bayan amincewa da tsagaita wuta ta tsawon kwanaki ukku a yakin da ake gwabzawa kasar,wadda ta fara aiki a jiya.

Shugabar Hukumar  kula da ‘Yan Najeriya mazauna kasashen ketare, Uwargida  Abike  Dabiri Erewa,  ta tabbatar da cewar  gwamnatin taraiyya ta  fitar da naira milyan 150 domin yin hayar manyan motoci  guda 40, wadanda zasu dauke  ‘yan Najeriyar da suka makale a kasar  domin tsallakar dasu zuwa kasar Masar.

Rahotanni sun baiyana cewar  Babban bankin kasa ta hannun Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa,Ya saka kudin ta cikin wani asusun kanfanin zirga-zirgar ababen hawa  da ba’a baiyana sunansa ba, domin fara kwashe  mutanen daga safiyar yau.

A  yanzu haka kasashen waje  na amfani da  tsagaita wutar da aka samu wajen kwashe ‘yan kasashensu da suka makale a kasar ta Sudan, wadda  ta fada cikin  rikici.