On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

Gwamnatin Taraiyya Ta Samu Nasarar Karbo Sama Da Naira Bilyan 3 Na Kudaden Da Aka Sace A Najeriya

KUDI

Gwamnatin taraiyya ta samu nasarar karbo sama da naira Milyan Dubu 3 da Milyan 200 da aka sace daga kasar nan, ta hanyar yin shari’oi daban daban da aka yi a fadin duniya, daga cikin watan Maris din shekara 2021 zuwa watan Mayun 2022.

Kazaalika rahotanni sun baiyana cewa  gwamnatin taraiyya ta samu zarafin  tattara sama  da naira bilyan 1 da milyan 82 daga kadarorin sata da aka siyar  a cikin watanni  18  na farkon  gwamnatin shugaban kasa Buhari.

Ministan shari’a na kasa Abaubakar malami ne ya baiyana haka  yayin zantawarsa da manema Labarai  na fadar shugaabn kasa.

Ya ce  tuni aka yi amfani da kudaden   wajen gudanar  da aiyukan raya kasa.