On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Gwamnonin APC Sun Magantu Akan Murabus Din Shugaban Jam'iyyar Da Sakatarenta

Gwamnonin Jam’iyyar APC sun magantu akan saukar Sanata Abdullahi Adamu daga shugabancin jam’iyyar da kumasakatarensa Sanata Iyiola Omisore, suna masu cewa sun dauki matakin ajiye mukaman bisa radin kansu.

Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Imo Hope Uzodinma shine ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema la Abuja.

Hakan na zuwa ne yayinda gwamnonin sukayi alkawarin cewa za’a magance matsalar tsadar rayuwa da ake fuskanta ta hanyar karin farashin ma da kayan abinci.