On Air Now

Off Air

Midnight - Noon

Hukumar EFCC Zata Gurfanar Da Tsohon Babban Akanta Na Kasa Ahmed Idris Gaban Kotu

AHMED IDRIS

A yau ne hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, za ta gurfanar da tsohon Babban Akanta na kasa, Ahmed Idris a gaban Kotu.

Kakakin Hukumar  EFCC, Mista Wilson Uwujaren shine  ya  tabbatar da haka  ta wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, a Abuja babban birnin taraiyya. Ya ce za a gurfanar da Idris da wasu mutane uku a gaban mai shari’a Adeyemi Ajayi na wata babbar kotun birnin tarayya Abuja.

Ya ce sauran Mutane ukun da za’a  gurfanar  tare da tsohon Babban Akanta na kasa   bisa zarginsu da wawure tsabar kudi har  Naira biliyan 109 sun hada da Godfrey Akindele da Mohammed Usman  sai kuma  kasuwar  zamani  ta  Gezawa Market and Exchange Limited.

A cewarsa, za a gurfanar da wadanda ake zargin ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume 14 da suka hada da sata da kuma  cin  amana.

 Sanarwar ta yi zargin cewa tsohon babban akanta na kasa  Ahmed Idris ya kwashe kudaden ne ta hanyar  amfani da wasu kwararrun kanfanonin tuntuba na bogi  da kuma wasu ayyukan da ba su dace ba ta hanyar amfani da ‘yan uwansa da kuma Makusanta.

A wani bangaren kuma, Wasu Rahotanni na baiyana  cewa  tsohon Babban Akanta na kasa da aka  dakatar, Ahmed Idris,  Ya karbi cin hancin  Naira biliyan 15, domin a hanzarta bin diddigin kaso 13 bisa 100  na kudaden albarkatun man fetir da ake bawa   jihohin da ke hako mai a kasar nan.

A bisa tsari ana  bawa jihohin kaso 13 bisa 100 na kudaden da ake samu daga bangaren man da ake hakowa a jihohin.

A cewar EFCC, Idris ya karbi kudin daga hannun Olusegun Akindele, domin ganin anyi gaggawar bawa jihohin kudin

Akindele ya kasance  mataimaki na musamman ga babban  Akantan  tsakanin  watan  Fabrairu  zuwa  Nuwambar 2021.