On Air Now

Off Air

Midnight - 5:00am

HukumarYaki Da Cin Hanci Ta Fara Gwanjon Kadarorin Data Kwace Daga Masu Karbar Rashawa

ICPC

Hukumar yaki da cin hanci da kuma karbar rashawa ta kasa ICPC, Ta bude baje kolin gwanjojin kayayyakin da aka kama a bana, wanda aka mallakawa gwamnatin taraiyya su.

Mai magana da yawun hukumar uwargida, Azuka Oguguwa ce  ta baiyana haka ta cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin a  Abuja.

Ta Ambato shugaban hukumar, Farfesa Bolaji Owasanaye na alkawarin cewar  za’a gudanar da aikin a faiyace batare da wata ‘kunbiya-‘kunbiya ba.

Daga  nan sai ya yabawa masu  sayen gwanjon kayayyakin saboda hadin kan da suke bawa  hukumar, ya kuma sake basu tabbacin cewar  za’a  yi baje kolin a  bude  batare  da wani ‘boye boye ba.