On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Jam'iyyar APC Ta Ce Peter Obi Ba Halastaccen Dan Jam'iyyar Labour Bane

PETER OBI

Jam’iyyar APC ta kammala shirya shaidu da kuma hujjojin bada kariya akan karar da Peter Obi na jam’iyyar Labour ya shigar gaban kotu, inda yake kalubalantar yadda sakamakon zaben shugaban kasa da aka yi ranar 25 ga watan Fabarairun bana ya kasance.

A wani martani da  jam’iyyar ta APC  ta  hannun Lauyanta  Thomas Ojo  ya gabatar,Ya baiyana cewar  dan takarar  shugaban kasar  na jam’iyyar  Labour,ba cikakken  dan jam’iyyar  ba ne har  zuwa lokacin da aka yi zabe.

Bugu da kari jam’iyyar  ta APC  ta baiyana cewar  tsohon gwaman  na Anambra  dan jam’iyyar  PDP  ne har  zuwa  ranar 24  ga watan Mayun 2022,kuma  an  tantance  shi a  matsayin daya daga cikin masu neman takarar  shugabancin kasar nan a karkashin jam’iyyar  ta PDP, a cikin watan Afrilun 2022.

A saboda haka  jam’iyyar ta APC ta  ce  Peter  Obi bai cancanci  ya kalubalanci sakamakon zaben shugaban kasa ba.