On Air Now

Maraicen Asabar

6:00pm - Midnight

Kanfanin Mai Na Kasa Ya Ce Za'a Samu Saukin Karancin Mai Daga Makon Gobe

NNPC

Kanfanin mai na kasa ya ce ba zai iya bada tabbacin cewar ba za’a samu dogayen layukan ababen hawa a gidajen mai ba.

Shugaban kanfanin  Mele  Kyari   wanda ya  baiyana haka a ranar  Talata,   ya  zargin  cewar   dogayen  layukan  ababen  hawan  da ake  samu  nada  nasaba da yadda  masu  son cin riba  a dare   daya  ke  gudanar  da harkokinsu.

A  hirarsa  da  gidan  Talabijin na kasa , Mele Kyari  ya yi  alkawarin cewar  za’a  samu  saukin  karancin  man  da  ake samu daga  makon gobe.

To sai dai kuma  bai bada tabbacin  cewar   za’a karshen  matsalar   dogayen  layukan ababen  hawar  nan bada  jimawa  ba.

Ya  kara  da cewa  Najeriya  na bukatar  zunzurutun kudi har naira  tiriliyan Hudu  da  bilyan  27  domin  ta warware  dukkanin wasu  bukatu  da suka  shafi  tallafin mai.