On Air Now

ZANGON BARKA DA SAFIYA

5:00am - 10:00am

Kaso 76% Na 'Daliban Da Suka Rubuta Jarabawar WEAC Sun Yi Nasara

Hukumar shirya jarabawar kammala karatun sakandire ta yammacin Afirka WEAC ta fitar da sakamakon jarabawar watan Mayu zuwa Yuni.

Yayinda aka fitar da sakamakon a jiya litinin, hukumar WEAC tace dalibai milliyan 1 da dubu dari 2 da 22 da 505 kwatankwacin kasha 76 da digo 36 na jimillar daliban sun samu nasara a darussa biyar ciki harda Turanci da Lissafi.
Wannan alkaluma sun nuna an samu koma baya da kasha biyar cikin dari idan aka kwatanta da kasha 81 da digo 7 da jimillar daliban da suka samu nasara a darussa biyar yayin jarabawar ta shekarar 2021.

Da yake sanar da sakamakon jarabawar jiya litinin a legas, shugaban hukiumar WEAC a Najeriya, Patrik Areghan yace an rike sakamakon dalibai dubu dari 3 da 65 da 564 sakamakon samunsu da laifuka masu alaka da satar jarabawa.