On Air Now

ZANGON SAFIYAR LAHADI

5:00am - Noon

Kotu Ta Datse Igiyar Auren 'Yar Gwamnan Kano Ganduje

ASIYA GANDUJE DA TSOHON MAI GIDANTA

Wata babbar kotun shari'ar musulunci dake zamanta a nan Kano, ta datse igiyar auren Asiya Abdullahi Umar Ganduje da Maigidanta Inuwa Uba, ta hanyar yin Khul'i a tsakaninsu.

Asiya Ganduje wadda ta kasance  'yar  gwamnan jihar Kano, ta garzaya  kotun ta hannun  lauyanta, inda  take neman  kotun  ta kawo karshen auren dake tsakaninta da mijinta, inda ta baiyana cewar zata mayar masa da sadakin da ya  bata naira dubu hamsin.

Da  yake yanke  hukuncin, Mai shari'a Mallam Abdullahi Halliru, Ya  ce hujjojin da aka gabatar a zaman shari'ar  sun tabbatar da cewar  mai karar  ta karbi naira dubu hamsin.

Sai dai a nasa bangaren Lauyan wanda ake kara, Umar I Umar, Ya yi fatan kotun zata bashi  dukkanin wasu bayanai na yadda zaman kotun ya kasance, inda  ya ce  yana da sha'awar  zasu daukaka kara zuwa kotun sama, bayan sun tattauna  da wanda  yake karewa Inuwa Uba.

A hirarsa da wakilinmu Bashir Faruk Durumin Iya, Lauyan mai kara, Barister  Ibrahim  Aliyu Nasarawa, Ya  ce  kotun  ta raba auren ne  bisa  tsarin  shari'ar  musulunci.