On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Kotu Ta Umarci Bacineshen Da Ake Zargi Da Halaka Ummita Ya Samo Wanda Zai Yi Masa Tafinta A Kotu

DAN CHINA

Wata babbar kotu mai lamba 17 dake zamanta a Miller Road karkashin mai shari’a Ado Ma’aji ta Umarci Ofishin jakadancin kasar Sin, Da ya samo wanda zai yiwa Bacanishen nan da ake zargi da halaka Ummukulsum Sani Buhari, Kisan gilla, Wanda zai yi masa tafinta a gaban kotu.

A lokacin da aka cigaba da zaman kotun  a yau,  Wanda ake tuhumar  ya baiyana gaban kotun tare da lauyansa, Barrister Balarabe  Muhammad Dan Azumi,  Ya bukaci kotun da   ta samar da wanda  zi yiwa Bacanishen  tafinta daga harshen turanci zuwa  Sinanci, bisa ga dogaro da sashi na 36, 6 cikin baka da A Sai B da E na kundin tsarin mulkin kasa sashi na 237, 2 cikin baka na dokar aikatar Lefuka.

Kazalika shima babban lauyan gwmanati, kuma kwamishinan shari’a Barrister  Musa Abdullahi Lawal, Yace duk da kasancewar Lauyan wanda ake kara ya bukaci samun tafinta akan lamarin, amma a baya, wanda ake tuhumar yayi magana da turanci a zaman kotun na baya, Inda yace  zasu rubutawa  ofishin jakadancin kasar China dake nan Najeriya  wasika domin samar da wanda  zai yi masa tafintar kafin nan da makwanni ukku lokacin   da kotun zata sake yin zama.

Wakilinmu Bashir Faruk Durumin Iya, Ya labarta mana cewa, Mai shari’a Ma’aji ya dage zaman kotun zuwa ranar  27 ga watan Octoban da muke ciki, Sannan kuma ya bada umarnin cigaba da tsare wanda ake tuhuma a gidan gyaran hali.