On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Kotu Ta Kori Bukatar Cigaba Da Rajistar Masu Kada Kuri'a A Najeriya

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ki amincewa da bukatar umartar hukumar zabe ta kasa INEC da ta dawo ci gaba da gudanar da rajistar masu kada kuri’a.

Mai shari’a Inyang Ekwo ya ki amincewa da bukatar a jiya a bisa hujjar cewa kwanaki kalilan ne suka rage na yin rijistar kamar yadda doka ta tanada.

Alkalin ya ce zuwa ranar yanke hukuncin, babu kwanaki masu yawa fin a kai lokacin da kwanaki 90 zasu ragewa INEC ta  gudanar da babban zabe.

Wadanda suka kai karar INEC sun hada da Anajat Salmat da Earnest Stanley da Cif Charles Okafor da Mista Samuel Oluwakemi.

Sun bukaci kotun da ta umurci INEC da ta dawo cigaba da rajistar masu kada kuri’a wadda ta dakatar  kwanaki 208 kafin zaben 2023.

 A farkon korafin da suka gabatar a gaban kotun, masu shigar da kara sun ce lokaci bai yi ba da  INEC zata  dakatar da cigaba da rajistar katin  zabe  sabanin yadda kundin tsarin mulki ya tanada. 

Sun bukaci kotun da ta umarci hukumar zaben da ta gaba da gudanar da aikin rajistar kamar yadda dokar kasa ta tanada.