On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Kungiyar Kwadago A Najeriya Na Shirin Kiran Taron Kasa Kan Karin Farashin Man Fetur

Ana cigaba da martani akan  karin farashin man fetur daga Naira 540 zuwa Naira 617 kowace lita a Najeriya, yayinda ma’ajin kungiyar kwadago ta kasa NLC, Hakeem Ambali  ya fadawa  manema labarai cewa kungiyar za ta kira taron majalisar zartarwarta na kasa biyo bayan karin farashin.

Da yake magana a  gidan talabijin, shugaban kungiyar kwadago ta kasa NLC, Joe Ajaero, ya ce ana yaudarar ‘yan Najeriya kan batun farashin man fetur.

 

Tun da farko, shugaban kungiyar kwadago ta kasa a jihar Rivers, Alex Agwanwor, ya shaidawa gidan Radiyon Nigeria Info cewa kungiyar zata shirya yajin aikin a fadin kasarnan saboda sabon farashin man fetur.

Har ila yau, jam'iyyar PDP ta bayyana karin farashin man fetur na baya-bayan nan amatsayin tunzura ‘yan kasa da kuma gayyatar rikici a fadin kasarnan.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba a cikin wata sanarwa da ya fitar, yace tsarin farashin man Fetur a halin yanzu tsantsar rashin tausayi ne, yana mai zargin cewa gwamnati na son mutanen da  suka Tagaiyyara saboda tsananin wahala.