On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Kungiyar Kwadago Ta Gindayawa Gwamnati Wasu Sharudda Kafin Yiwa Ma'aikata Karin Albashi

NLC

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC sun gindaya wadansu sharudda akan batun sake sake duba mafi karancin albashi na kasa.

Kungiyoyin sun baiyana cewa, sun dauki matakin ne la’akari da  yadda hauhawar farashin kayayyaki ke ci gaba da yin ‘kamari, da  kuma faduwar darajar Naira wanda dole ne a yi   la’akari dasu, kafin yin wata magana  ta  karin albashin da gwamnatin tarayya ta sanar.

Kungiyar kwadagon ta bayyana cewa kusan duk farashin wani kayan masarufi da ake amfani dashi a kasar nan  ya  tashi, inda ta  baiyana cewa muddin aka cigaba da tafiya a haka, to babu wani karin albashi da zai gamsar da ma’aikatar kasar nan.

Kungiyoyin kwadago  na  NLC da TUC sun baiyana haka ne a matsayin martani ga  kalaman da Ministan Kwadago da  nagartar aiki  Chris Ngige ya  yi, inda  ya  bayyana cewa nan ba da dadewa ba Gwamnatin Tarayya za ta bayyana karin albashi ga ma’aikatan gwamnati saboda karuwar farashin kayayyakin masarufi.