On Air Now

Off Air

Midnight - Noon

Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Caccaki Shawarar Da Gwamnoni Suka Bayar Na Sallamar Ma'ikatan Da suka Haura Shekara 50

TAMBARIN KUNGIYAR KWADAGO

Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta yi Allah wadai da shawarar da gwamnonin jihohi suka bayar na neman gwamnatin tarayya ta kori ma’aikatan da suka haura shekara 50 tare da sanya haraji kan ‘yan Najeriya da suke da kudi sama da naira Dubu 30.

Domin shawo kan tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan, gwamnonin sun bayar da shawarar  cire tallafin man fetur.

Kazalika an ce sun roki Shugaban kasa Muhammadu Buhari  ya mayar da bashin da ake bin kasar nan na Naira Tiriliyan 19 zuwa tsarin biyan bashi ta hanyar tsarin  hannun jari wanda zai dauki  tsawon shekaru 100,  sannan kuma  ya rage ayyukan da Kamfanin Mai na kasa ke  gudanarwa  da kuma rage ayyukan mazabu da  ‘yan majalisa ke gudanarwa da sauransu.

To sai dai shugaban kungiyar kwadago ta kasa  NLC, kwamared  Ayuba Wabba, ta cikin  wata wasika da ya aike wa shugaban kasa mai kwanan wata 8 ga watan Agustan da muke ciki, ya ce shawarar da gwamnonin suka  gabatar  tsantsar son kai ne  da rashin sanin ya kamata  tare da rashin yin duba kan halin da mutanen kasa suke a ciki.