On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Kungiyar ASUU Zata Sake Ganawa Da Wakilan Gwamnatin Taraiyya A Yau Litinin

WAKILAN ASUU DANA GWAMNATIN TARAIYYA

A yaune Kungiyar Malaman Malaman Jami’oi ta kasa ASUU, zata sake ganawa da wakilan gwamnatin taraiyya akan dambawar yajin aikin da suke kan yi wanda yanzu haka yake cikin wata na shida da somawa.

Shugaban Kungiyar na kasa, Farfesa  Emmanuel  Osodeke, Yace ganawar da zasu sake yi zata mayar da hankali ne kan yarjejeniyar da suka kulla tsakaninsu da gwamnatin taraiyya a shekarar  2009.

Kazalika yace bukatunsu basu tsaya  ga iya maganar tsarin biyansu albashi ba,  harma da abubuwan da suka shafi samar da sabon tsari  na gudanar da jami’oi  da  basu damar cin gashin kansu, da kuma samar da kudaden   tafiyar da jami’oin.

Sai dai kuma shugaban kungiyar  jami’oin ta kasa  yace  gwamnatin taraiyya ta takaita bukatun nasu ga iya maganar  yadda ake biyansu albashi, Yace  idan har  ganawar da zasu yi a yau ta haifar da ‘Da Mai Ido, To Babu shakka zasu janye yajin aikin da suke yi.