On Air Now

ZANGON RANA

10:00am - 3:00pm

Kungiyoyin Kwadago Sun Koka Kan Cigaba Da Tsadar Farashin Kayayyaki A Kasar Nan

shugabancin kungiyar kwadago ta NLC da kuma TUC sun nuna damuwarsu kan yadda ake ci gaba da fama da tsadar farashin kayayyaki a kasar nan.

Kungiyoyin sun koka da cewa karancin man fetur  ya kara haifar da wata tsadar rayuwa ga jama’ar kasar nan.

A wata sanarwa da kungiyoyin biyu suka raba wa manema labarai a Abuja ranar Juma’a, sun zargi gwamnati da laifin karin farashin man fetur da kuma haddasa  karancin sa.