On Air Now

ZANGON DARE

8:00pm - Midnight

Ma’ikatan Kamfanin Rarraba Lantarki Na Kano KEDCO Sun Bada Wa’adin Tsunduma Yajin Aiki

Ma’aikatan Lantarki a karkashin Kungiyar Ma’aikatan Lantarki ta Kasa, NUEE, sun fitar da sanarwar wa’adin kwana 14 a shirye-shiryen tsunduma yajin aiki ga mahukuntan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano, KEDCO, kan kudaden fansho da ake yankewa ba tare da turawa kamfanonin Asusun Fansho ba, da sauran matsaloli.

Ma’aikatan sun yi barazanar gurgunta ayyukan kamfanin da ake rarraba lantarki idan har hukumar ta kasa yin abin da ya dace.

Jaridar Solacebase ta  rawaito  cewa a cikin wata takarda ga Manajan Darakta kuma  Babban Jami'in kamfanin tare da kwafi ga shugaban hukumar tsaro ta DSS da Babban Sakatare na kungiyar ma’aikatan lantarki NUEE, Joe Ajaero, sun  koka da yadda KEDCO ke cigaba da bijirewa tsarin aikewa kamfanonin fansho kudaden da ake yankewa ma’aikatan tare da sauran matsaloli da suka shafi harkokin kwadago.

Idan za a iya tunawa, kwamitin da aka  kafa da ke bin diddigin biyan bashin da ma’aikatan  KEDCO ke bi wanda ya ba da shawarar tsarin biyan kudin a cikin watanni hudu, ya mika rahotonsa ta cikin wata takarda mai kwanan wata 21 ga Janairu na  2022, yana mai cewa A taron da aka gudanar a ranar 30 ga Maris  tsakanin kungiyar da hukumar KEDCO kan jinkiri wajen aiwatar da rahoton kwamitin hukumar ta yi alkawarin fara biyan kudaden  ba tare da bata lokaci ba.

Sai dai abin takaici acewar ma’aikatan   shugaban kamfanin na KEDCO ya ki dawowa daga Abuja a lokacin da aka rike kudaden kungiyar ma’aikatan  na watanni 12, sai basussukan fansho na watanni 56  da sauran batutuwan da suka shafi ma’aikata.