On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Majalisar Dattawa Zata Binciki Yadda Aka Rabawa Alkalai Bashin Naira Bilyan 10

ALKALAI

Majalisar dattawa ta tuhumi ma’aikatar shari’a kan rashin bada cikakken bayani kan yadda  aka  raba  bashi wasu  kudade  har Naira biliyan 10 da milyan dari  4 a tsakanin Alkalan kasar nan.

Tuhumar  ta biyo  bayan nazarin rahoton kwmaitin  kula da baitul malin gwamnati na shekarar  2017 da 2018 karkashin jagorancin Sanata Matthew Urhoghide, da majalisar  ta  yi.

Kwamitin ya yi binciken ne  ta hanyar amfani da rahoton tantance  kididdigar  kudi  da ofishin babban mai binciken kudi na tarayya ya mika wa majalisar.