On Air Now

ZANGON SAFIYAR LAHADI

5:00am - Noon

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Dokar Kula Da Lafiyar Mata Masu Dauke Da Juna Biyu Da Kananan Yara

MAJALISAR DOKOKIN JIHAR KANO

Bayan shafe shekara bakwai ana fadi tashin tabbatar da kudirin wata doka, A yanzu haka zauren majalisar dokokin jihar Kano ya amince da kudirin dokar kula da mata masu dauke da juna biyu da kuma kananan yara, a wani mataki na kawo karshe yawan mace-macen mata da ake samu a lokacin haihuwa.

Shugaban kungiyar kare hakkin Dan  hakkin da  Adam da kuma wayar da kan jama’a,Dr  Ibrahim  Zikirullahi  wanda  kungiyarsa  ce  ta bijiro da kudurin dokar, kuma  wani  Dan  majalisa  ya gabatar da kudirin,  shi  ne ya  tabbatar da amincewar  kudirin a matsayin doka  a  ranar Laraba.

Ya fadawa manema  Labarai  cewar  dokar  an samar da ita ne  domin ta karfafa  dokar  bangaren zartawa  ta  kula da mata masu dauke da juna biyu da kananan yara,  wadda  tsohon gwamnan jihar kano Rabiu Musa  Kwankwaso  ya bullo da  ita  a shekarar  2001.

A cewarsa idan har  gwamnan jihar Kano  Abdullahi Umar Ganduje ya sa hannu  kan dokar kafin  saukarsa  daga kan mulki, Zata temaka wajen inganta kula da lafiyar  masu karamin  karfi a  jihar kano.

Daga  nan sai ya yabawa  zauren majalisar dokokin jihar  da sauran abokan hulda  wadanda  suka aiki ka fada  da ka fada domin samun tabbatuwar dokar,  Yana mai cewar  tarihi ba zai manta da gwamna  Ganduje ba idan har ya sa hannu kan dokar  kafin ranar  29 ga watan da muke ciki.