On Air Now

ZANGON MARAICE

3:00pm - 8:00pm

Makarantu Masu Zaman Kansu Zasu Kara Kudin Makaranta Saboda Janye Tallafin Mai

Kungiyar masu makarantu dake zaman kansu ta kasa ta ce janye tallafin mai da gwamnatin taraiyya ta yi zai sa ta kara yawan kudin makaranta dake take karba daga hannun iyayen yara.

Shugaban kungiyar Chief Yomi Otubela shi  ne  ya baiyana haka yayin wani taro da aka shirya kai tsaye  ta allon gani gaka,  kan batun cire tallafin mai , Ya ce duk wani sauyi da za’a samu kan  farashin man fetir  zai shafi yadda suke  gudanar da harkokinsu.

Ya kara da cewar  matsalar  ba zata tsaya ga iya makarantu  masu zaman kansu ba, kasancewar  matsala ce  da  ta shafi  al’umma baki daya.

Kazalika kungiyar ta yi kira ga  gwamnati data samar da matakan  bada tallafin rage radadin janye  tallafin ga  ‘yan  kasa.